Alkalin Babbar Kotun Jiha dake Bauchi, Mai Shari’a Aliyu Baba Usman, ya baiwa Hukumar (EFCC) damar ci gaba da bincike a kan Alhaji Hamza Koshe da kamfaninsa mai suna Pentech Engineering Nig. Ltd.
Rahotanni sun bayyana cewa a ranar 23 ga Satumba, 2024, Koshe ya shigar da kara a kotu yana neman a hana EFCC ta ci gaba da bincike da gurfanar da shi tare da kamfaninsa.
Yayin yanke hukunci a ranar 30 ga Yuli, 2025, Mai Shari’a Usman ya bayyana cewa: “Wannan kotu da sauran kotunan shari’a ba su da hurumin hana hukumomin tsaro da doka gudanar da ayyukansu na bincike da gurfanarwa, musamman a kan laifukan rashawa, almundahana, halatta, da sauran manyan laifukan tattalin arziki.”
Saboda haka, kotu ta baiwa EFCC damar ci gaba da bincike a kan Koshe.
Tun da farko EFCC ta gayyaci Koshe domin amsa tambayoyi, amma maimakon ya amsa, sai ya garzaya kotu ya shigar da kara.
–Zamani TV







