- YANZU-YANZU: Kotu ta wanke dan sanda Abba Kyari daga gaba daya tuhume-tuhumen da ake masa
- Residents of Styre Quarters, Zango behind IDC in Bauchi Local Government Area of Bauchi State have continued to call on governments at all levels to come to their aid.
- Ana zargin wasu ‘yan bindiga da kashe wani shugaba a ƙauyen Zalau, cikin Ƙaramar Hukumar Toro ta Jihar Bauchi
- Ana zargin wasu ‘yan bindiga da kashe wani shugaba a ƙauyen Zalau, cikin Ƙaramar Hukumar Toro ta Jihar Bauchi,
- Wunti Al-Khair Foundation ta ƙaddamar da shirin ƙarfafa matasa kan fasahohin neman aiki da ƙirƙirar kasuwanci
- Majalisa ta amince a ƙirƙiro jihohi shida a Najeriya
- ‘Yan Sanda Sun Cafke Wanda ake Zargi da Kashe Mawakin Gargajiya
- Kotu Ta Sanya Ranar 30 ga Oktoba Don Gurfanar da Mutum 5 da Ake Zargi da Cin Mutuncin Sanata Shehu Buba a Intanet
Author: Zamani TV
YANZU-YANZU: Kotu ta wanke dan sanda Abba Kyari daga gaba daya tuhume-tuhumen da ake masa
Mai Shari’a James Omotosho na Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ya sallami tare da wanke dakatararren Mataimakin Kwamishinan ‘Yan Sanda, Abba Kyari, daga tuhume-tuhume guda 23 na zargin rashin bayyana kadarori da Hukumar National Drug Law Enforcement Agency (NDLEA) ta shigar a kansa. An gurfanar da Mista Kyari tare da ‘yan’uwansa guda biyu, inda ake zarginsu da rantsuwa kan takardun shaida na karya domin ɓoye asalin wasu kadarori. A cikin hukuncinsa, Mai Shari’a Omotosho ya bayyana cewa NDLEA ta gaza gabatar da isassun hujjoji da za su tabbatar da zarge-zargen, musamman dangane da batun rashin bayyana filayen kadarori. Kotun…
Residents of Styre Quarters, Zango behind IDC in Bauchi Local Government Area of Bauchi State have continued to call on governments at all levels to come to their aid.
The residents say they are disturbed by the lack of an access road to their homes, especially during the rainy season, due to the condition of a local bridge in the area which is currently inaccessible. The bridge was washed away in 2025 after a heavy downpour, leaving motorists stranded and unable to access their homes. As a result, residents have had to improvise by taking a longer route through the Bauchi Furniture Company–Gudun area before connecting to another road that leads to their homes. Abdulqadir Bala, a resident of the community, described the situation as devastating and disturbing. “We…
Ana zargin wasu ‘yan bindiga da kashe wani shugaba a ƙauyen Zalau, cikin Ƙaramar Hukumar Toro ta Jihar Bauchi
Ana zargin wasu ‘yan bindiga da kashe wani shugaba a ƙauyen Zalau, cikin Ƙaramar Hukumar Toro ta Jihar Bauchi, Alhaji Muhammad Bakoshi, yayin wani hari da suka kai wa garin. ‘Yan bindigar sun kuma sace daya daga cikin matan shi, Hannatu Muhammad, yayin harin da aka kai a daren ranar. Wani mazaunin yankin, Shamsuddeen Hashimu Zalawa, ya shaida wa Daily Trust cewa, ‘yan bindigar da adadinsu ba a tabbatar ba, sun shiga ƙauyen da misalin tsakar dare, suka harbi bindigogi sama, wanda ya janyo tsoro da rudani a cikin al’umma. Harin ya bayyana a fili cewa an kai shi…
Ana zargin wasu ‘yan bindiga da kashe wani shugaba a ƙauyen Zalau, cikin Ƙaramar Hukumar Toro ta Jihar Bauchi,
Ana zargin wasu ‘yan bindiga da kashe wani shugaba a ƙauyen Zalau, cikin Ƙaramar Hukumar Toro ta Jihar Bauchi, Alhaji Muhammad Bakoshi, yayin wani hari da suka kai wa garin. ‘Yan bindigar sun kuma sace daya daga cikin matan shi, Hannatu Muhammad, yayin harin da aka kai a daren ranar. Wani mazaunin yankin, Shamsuddeen Hashimu Zalawa, ya shaida wa Daily Trust cewa, ‘yan bindigar da adadinsu ba a tabbatar ba, sun shiga ƙauyen da misalin tsakar dare, suka harbi bindigogi sama, wanda ya janyo tsoro da rudani a cikin al’umma. Harin ya bayyana a fili cewa an kai shi ne…
Wunti Al-Khair Foundation ta ƙaddamar da shirin ƙarfafa matasa kan fasahohin neman aiki da ƙirƙirar kasuwanci
Gidauniyar Wunti Al-Khair Foundation (WAKF) ta gudanar da wani muhimmin shiri mai taken “Skills for Employability and Entrepreneurship Skills for a Changing World”, domin ba matasa damar koyon fasahohin da za su taimaka musu wajen samun ayyukan yi da kuma shiga harkar kasuwanci cikin nasara. An gudanar da taron ne a Bauchi, inda Malam Murtala Muhammad Alamai, Daraktan Cibiyar Kula da Ayyukan Neman Aiki (Career Services) na Federal Polytechnic Bauchi, ya gabatar da jawabin babban bako. Ya jaddada muhimmancin koyon sabbin fasahohi, kirkire-kirkire da jarumtaka wajen fuskantar sauye-sauyen tattalin arzikin zamani. A jawabin maraba da ya gabatar, Ango Mustapha, Daraktan…
Haɗaɗɗiyar kwamitin majalisar dattawa da ta majalisar wakilai ta tarayya kan gyaran kundin tsarin mulkin Najeriya ta amince da buƙatar ƙirƙirar sabbin jihohi guda shida a faɗin ƙasar. Wannan matsaya ta fito ne a ƙarshen taron ƙara wa juna sani na kwana biyu da aka gudanar a jihar Legas, ƙarƙashin jagorancin mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Barau I. Jibrin, tare da mataimakin shugaban majalisar wakilai, Benjamin Kalu. A cewar rahoton jaridar Daily Trust, kwamitin ya tattauna ne kan buƙatu 69 da suka haɗa da ƙirƙirar jihohi 55 da kuma ƙananan hukumomi 278. Daga cikin waɗannan buƙatun, kwamitin ya amince da…
‘Yan sanda a ƙaramar hukumar Tafawa Balewa ta jihar Bauchi sun kama wani mutum da ake zargi da hannu a kisan fitaccen mawaki, John Zuya Zuya, wanda ya shahara a tsakanin al’ummar Sayawa. Rahotanni sun bayyana cewa marigayin ya rasu ne bayan dawowarsa daga Lagos, inda ya gudanar da wani gagarumin bikin nishadi tare da masoyansa. Ana zargin wani abokinsa mai suna Emmanuel Wakili da kisan, bisa rahotannin da ke cewa an samu sabani tsakaninsu saboda kishi. Hukumar ‘yan sanda ta tabbatar da cewa bincike na ci gaba domin gano cikakken abin da ya faru.
Kotu Ta Sanya Ranar 30 ga Oktoba Don Gurfanar da Mutum 5 da Ake Zargi da Cin Mutuncin Sanata Shehu Buba a Intanet
Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta sanya ranar 30 ga Oktoba, 2025 domin gurfanar da wasu mutane biyar da ake zargi da aikata laifin cin mutuncin Sanata Shehu Buba Umar ta kafafen sada zumunta. Sanatan shi ne shugaban Kwamitin Majalisar Dattawa kan Tsaro da Leken Asiri. An shirya gurfanar da su a gaban Mai Shari’a Rita Ofili-Ajumogobia a ranar Talata, inda ake sa ran za su bayar da amsar tuhume-tuhumen da ake musu. Sai dai, rashin halartar alkalin ya sa aka dage shari’ar zuwa ranar 30 ga Oktoba. Lauyan gwamnati, Anthony Egwu, da lauyoyin wadanda ake tuhuma — Hamza…
Wani jigo a cikin matasan jihar Bauchi, Elder Karofi, ya yi kakkausar suka ga Sanata Shehu Buba bisa zargin yin amfani da mukaminsa wajen kama matasa a fadin jihar. A cikin wani faifan bidiyo da ya wallafa a safiyar yau, Elder Karofi ya zargi sanatan da amfani da karfin iko wajen tsoratar da matasa maimakon yin aiki tare da su don ci gaban siyasa da dimokuraɗiyya. Ya ce siyasa rigar ’yanci ce wacce ta baiwa kowa damar bayyana ra’ayinsa, ba doka ta kama ko tsoratar da mutane ba. “Shehu Buba, me kake nema da matasan Bauchi? Kullum sai ka kama…
Tsohon Shugaban Ƙungiyar Daliban ATBU Ya Soki Yunkurin Cire Kalmar “Technology” Daga Sunan Jami’ar
Tsohon Shugaban Ƙungiyar Daliban Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBU) Bauchi, Muhammad Aliyu wanda aka fi sani da Songuy, ya bayyana rashin amincewarsa da kudirin da ake yi na mayar da jami’ar daga ta kimiyya da fasaha zuwa jami’a ta gama-gari. Songuy ya bayyana wannan yunkuri a matsayin “mataki na komawa baya,” yana mai cewa duniya tana ci gaba cikin sauri ne saboda ci gaban fasaha da kere-kere. Ya ce ko da yake a Najeriya ana ganin jami’o’in gama-gari suna taimakawa wajen samar da ma’aikata da inganta tattalin arziki, amma gaskiyar magana ita ce fasaha ce ginshiƙin ci gaban duniya. “A…












