Author: Zamani TV

Zamani TV is a TV Station that brings you news about events happening in Nigeria and abroad, for the purpose of education, awareness and entertainment.

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta sanya ranar 30 ga Oktoba, 2025 domin gurfanar da wasu mutane biyar da ake zargi da aikata laifin cin mutuncin Sanata Shehu Buba Umar ta kafafen sada zumunta. Sanatan shi ne shugaban Kwamitin Majalisar Dattawa kan Tsaro da Leken Asiri. An shirya gurfanar da su a gaban Mai Shari’a Rita Ofili-Ajumogobia a ranar Talata, inda ake sa ran za su bayar da amsar tuhume-tuhumen da ake musu. Sai dai, rashin halartar alkalin ya sa aka dage shari’ar zuwa ranar 30 ga Oktoba. Lauyan gwamnati, Anthony Egwu, da lauyoyin wadanda ake tuhuma — Hamza…

Read More

Wani jigo a cikin matasan jihar Bauchi, Elder Karofi, ya yi kakkausar suka ga Sanata Shehu Buba bisa zargin yin amfani da mukaminsa wajen kama matasa a fadin jihar. A cikin wani faifan bidiyo da ya wallafa a safiyar yau, Elder Karofi ya zargi sanatan da amfani da karfin iko wajen tsoratar da matasa maimakon yin aiki tare da su don ci gaban siyasa da dimokuraɗiyya. Ya ce siyasa rigar ’yanci ce wacce ta baiwa kowa damar bayyana ra’ayinsa, ba doka ta kama ko tsoratar da mutane ba. “Shehu Buba, me kake nema da matasan Bauchi? Kullum sai ka kama…

Read More

Tsohon Shugaban Ƙungiyar Daliban Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBU) Bauchi, Muhammad Aliyu wanda aka fi sani da Songuy, ya bayyana rashin amincewarsa da kudirin da ake yi na mayar da jami’ar daga ta kimiyya da fasaha zuwa jami’a ta gama-gari. Songuy ya bayyana wannan yunkuri a matsayin “mataki na komawa baya,” yana mai cewa duniya tana ci gaba cikin sauri ne saboda ci gaban fasaha da kere-kere. Ya ce ko da yake a Najeriya ana ganin jami’o’in gama-gari suna taimakawa wajen samar da ma’aikata da inganta tattalin arziki, amma gaskiyar magana ita ce fasaha ce ginshiƙin ci gaban duniya. “A…

Read More

Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed, ya rattaba hannu kan wasu muhimman dokoki guda huɗu da nufin ƙarfafa tsarin mulki, inganta masarautu, da tabbatar da walwalar ma’aikata a fadin jihar. Daya daga cikin dokokin da aka amince da su ita ce soke dokar kafa Masarautar Sayawa da maye gurbinta da Masarautar Zaar, wacce za ta kasance da hedikwata a kauyen Mhrim Namchi da ke cikin ƙaramar hukumar Tafawa Balewa — domin amsa tsohon buƙatar al’ummar yankin. Haka kuma, Gwamna Bala ya sanya hannu kan Dokar Kafa da Dage Sarautu, wacce ta ba da dama ga ƙirƙirar sabbin masarautu guda…

Read More

Majalisar Dattawa ta amince da karatu na biyu na kudirin da ke neman sauya sunan Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa, Bauchi (ATBU), ta hanyar cire kalmar “Technology” daga cikinsa. Wannan mataki na nufin mayar da jami’ar ta zama jami’a ta gama-gari (conventional university) wacce za ta iya koyar da fannoni da dama, ciki har da shari’a (law), da sauran darussa da ba na fasaha ba. Wannan kudiri an gabatar da shi ne kuma ya samu cikakken goyon bayan Sanata Shehu Buba Umar, wanda ya bayyana cewa gyaran zai buɗe sabbin damar karatu da bunƙasa ilimi ga matasa a yankin arewa maso…

Read More

Kungiyar Ohanaeze Youth Council (OYC), wacce ita ce babbar kungiyar matasan Igbo a fadin duniya, ta sanar da tsawaita zanga-zangar neman a saki Nnamdi Kanu har zuwa ranar Asabar, 25 ga Oktoba, 2025, karkashin taken “Operation Occupy Abuja.” Kungiyar ta kuma yi kira ga gwamnati da ta saki duk masu zanga-zangar da aka kama cikin sa’o’i 24, tana gargadi cewa cigaba da tauye ‘yancin jama’a zai iya kara tayar da hankalin al’umma da jefa kasa cikin rashin kwanciyar hankali. Ohanaeze ta ce manufar wannan mataki ita ce nuna adawa da tsare Nnamdi Kanu ba tare da hukunci ba, tare da…

Read More

Kungiyar Concerned Citizens of Bauchi State ta aika da wata takardar ƙorafi zuwa ga Shugaban Jami’ar Sa’adu Zungur da ke jihar Bauchi, kan zargin wani malami a Sashen Shari’a (Faculty of Law) na jami’ar, da laifin cin zarafin mata, yin amfani da mukami ba bisa ka’ida ba, da kuma aikata rashin da’a ta fuskar aiki. A cikin takardar ƙorafin da ta ke ɗauke da kwanan wata 14 ga Oktoba, 2025, kungiyar ta bayyana cewa ta yanke shawarar sanar da jami’ar ne bisa zargin da ya daɗe ana yi wa malamin na yin lalata da dalibai mata da ke karatu a…

Read More

Wani mutum dan asalin jihar Ebonyi mazaunin jihar Lagos mai suna Comrade Jeremiah Obaji, wanda ya yi tattaki na tsawon kwanaki 17 daga Ikorodu dake jihar Lagos zuwa garin Abakaliki domin godewa Gwamna Francis Nwifuru kan yadda yayi silar dawowar zaman lafiya a yankin Effium, ya samu kyautar Naira Miliyan Goma daga wajen Gwamnansu na jihar Ebonyi. Mutumin dai yayi tafiyar kusan kilomita 600 ne a kafa, a tsawon kwanaki 17 da yayi a hanya sannan kuma ya samu kyakkyawar tarba a wajen jama’ar gari. koMutumin Da Ya Yi Tattaki A Yankin Kudu Ya Samu Kyautar Naira Milyan Goma Daga…

Read More

Hon. Mansur Manu Soro Ya Kafa Cibiyar Karatu ta NOUN a Soro, Jihar Bauchi Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Darazo–Ganjuwa, Hon. Mansur Manu Soro, ya kaddamar da sabuwar cibiyar karatu ta National Open University of Nigeria (NOUN) a garin Soro, Jihar Bauchi — wani babban ci gaba a fannin ilimi a yankin Bauchi da Arewa maso Gabas baki daya. Cibiyar, wacce aka gina a fili mai fadin kusan hektar 10, tana dauke da manyan gine-gine masu inganci da za su iya karbar dalibai fiye da 1,000 a matakin digiri. Hon. Soro ya bayyana cewa wannan cibiyar ita ce irinta…

Read More