Majalisar Dattawa ta amince da karatu na biyu na kudirin da ke neman sauya sunan Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa, Bauchi (ATBU), ta hanyar cire kalmar “Technology” daga cikinsa. Wannan mataki na nufin mayar da jami’ar ta zama jami’a ta gama-gari (conventional university) wacce za ta iya koyar da fannoni da dama, ciki har da shari’a (law), da sauran darussa da ba na fasaha ba.
Wannan kudiri an gabatar da shi ne kuma ya samu cikakken goyon bayan Sanata Shehu Buba Umar, wanda ya bayyana cewa gyaran zai buɗe sabbin damar karatu da bunƙasa ilimi ga matasa a yankin arewa maso gabas da ma ƙasa baki ɗaya.
Idan majalisar ta amince da kudirin a karatu na uku, hakan zai ba da damar hukuma ta sauya doka, kuma jami’ar za ta fara karɓar ɗalibai a sababbin fannoni da ba na fasaha kadai ba.







