Kungiyar Ohanaeze Youth Council (OYC), wacce ita ce babbar kungiyar matasan Igbo a fadin duniya, ta sanar da tsawaita zanga-zangar neman a saki Nnamdi Kanu har zuwa ranar Asabar, 25 ga Oktoba, 2025, karkashin taken “Operation Occupy Abuja.”
Kungiyar ta kuma yi kira ga gwamnati da ta saki duk masu zanga-zangar da aka kama cikin sa’o’i 24, tana gargadi cewa cigaba da tauye ‘yancin jama’a zai iya kara tayar da hankalin al’umma da jefa kasa cikin rashin kwanciyar hankali.
Ohanaeze ta ce manufar wannan mataki ita ce nuna adawa da tsare Nnamdi Kanu ba tare da hukunci ba, tare da nemi gwamnati ta mutunta doka da hakkin bil’adama.
Zanga-zangar ta ci gaba da samun karbuwa a sassa daban-daban na kasa, inda kungiyar ta bukaci matasa da su kasance cikin lumana yayin gudanar da tarukan su a Abuja da sauran manyan birane.







