Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta sanya ranar 30 ga Oktoba, 2025 domin gurfanar da wasu mutane biyar da ake zargi da aikata laifin cin mutuncin Sanata Shehu Buba Umar ta kafafen sada zumunta. Sanatan shi ne shugaban Kwamitin Majalisar Dattawa kan Tsaro da Leken Asiri.
An shirya gurfanar da su a gaban Mai Shari’a Rita Ofili-Ajumogobia a ranar Talata, inda ake sa ran za su bayar da amsar tuhume-tuhumen da ake musu. Sai dai, rashin halartar alkalin ya sa aka dage shari’ar zuwa ranar 30 ga Oktoba.
Lauyan gwamnati, Anthony Egwu, da lauyoyin wadanda ake tuhuma — Hamza Dantani da Affis Matanmi, sun halarci zaman kotun.
Sunayen wadanda ake tuhuma sun hada da:
- Ahmed Abdulrahman (41 shekara)
- Daure David (35 shekara)
- Ishaq Muhammad (25 shekara)
- Abdulrashid Musa (30 shekara)
- Nasir Abubakar (21 shekara)
An gurfanar da su ne bisa tuhume-tuhume 11, da Ofishin Sufeto Janar na ‘Yan Sanda (IGP) ya shigar da kara mai lamba FHC/ABJ/CR/526/2025, wadda aka rubuta ranar 3 ga Oktoba kuma aka karɓa ranar 6 ga Oktoba, 2025.
Tuhume-tuhumen sun shafi laifin cin mutunci ta kafar intanet (cyberstalking) da kuma zamba ta yanar gizo (advance fee fraud) bisa dokar Cybercrime Act 2015 (da aka gyara a 2024).
A cewar tuhumar farko, ana zargin su da yin yarjejeniya don aikata laifi na cin mutuncin Sanata Shehu Buba Umar ta hanyar intanet, wanda ya sabawa Sashe na 27(1)(b) kuma ake hukunta shi a ƙarƙashin Sashe na 21(1)(b) na dokar.
A cikin wani tuhunci na daban, ana zargin Ahmed Abdulrahman da yada wani bidiyo a TikTok da YouTube ta asusun “Kibanna Channel” inda ya zargi Sanatan da cewa “mai tallafa wa ‘yan ta’adda ne,” tare da yin kira da a bincike shi. Ana zargin ya san wannan zance ba gaskiya ba ne, amma ya aikata hakan don tayar da hankalin jama’a, sabanin Sashe na 24(1)(5) na dokar Cybercrime Act.
Haka kuma, Abdulrashid Musa da Nasir Abubakar, wadanda ake tuhuma na 4 da 5, sun nemi afuwa a bidiyo daban-daban da suka fitar bayan sun yarda da laifin cin mutuncin Sanatan Bauchi ta Kudu a kafafen sada zumunta.
Rahotanni sun nuna cewa hukumomi sun kammala bincike, kuma ana sa ran shari’ar za ta fara ne da karɓar amsar tuhume-tuhume daga wadanda ake zargi a ranar da kotu ta tsara — 30 ga Oktoba, 2025.








8 Comments
Pingback: tadalafil vidalista 60mg
Pingback: vidalista ct 20 mg
Pingback: prilosec omeprazole otc
Pingback: orlistat brand name
Pingback: zudena 100 mg
Pingback: sémaglutide oral nom commercial
Pingback: semaglutide nome commerciale puntura
Pingback: tadalafil female