Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Kaduna ta bayyana cewa ta kaddamar da bincike kan wani taron siyasa da tsohon gwamnan jihar, Malam Nasir El-Rufai ya shirya, wanda ya rikide zuwa tashin hankali da harbe-harbe.
SaharaReporters ta ruwaito cewa wasu ’yan daba da ake zargin gwamnatin jihar ta dauko su sun kai farmaki a wurin taron hada kan jam’iyyar Social Democratic Party (SDP) da African Democratic Congress (ADC) a cikin garin Kaduna, inda suka jikkata mutane da dama.
Rahotanni sun nuna cewa taron hadin gwiwar jam’iyyun SDP da ADC karkashin jagorancin Malam Nasir El-Rufai, tsohon gwamnan jihar, shi ne ya rikide zuwa tashin hankali har ya haifar da tarzoma da harbe-harben bindiga.







